Surah 51: Az-Zariyat — الذاريات
۞ قَالَ فَمَا خَطْبُكُمْ أَيُّهَا ٱلْمُرْسَلُونَ
(Ibrãĩm) ya ce: "To mẽne ne babban al'almarinku, yã kũ Manzanni!"
قَالُوٓا۟ إِنَّآ أُرْسِلْنَآ إِلَىٰ قَوْمٍۢ مُّجْرِمِينَ
Suka ce: "Lalle mũ, an aike mu zuwa ga waɗansu mutãne, mãsu laifi.
لِنُرْسِلَ عَلَيْهِمْ حِجَارَةًۭ مِّن طِينٍۢ
"Dõmin mu saka musu waɗansu duwãtsu na wani yumɓu (bom).
مُّسَوَّمَةً عِندَ رَبِّكَ لِلْمُسْرِفِينَ
"Waɗanda aka yi wa alãma daga wajen Ubangijinka, dõmin mãsu ɓarna."
فَأَخْرَجْنَا مَن كَانَ فِيهَا مِنَ ٱلْمُؤْمِنِينَ
Sa'an, nan Muka fitar da wanda ya kasance a cikinta daga mũminai.
فَمَا وَجَدْنَا فِيهَا غَيْرَ بَيْتٍۢ مِّنَ ٱلْمُسْلِمِينَ
Sai dai ba mu sãmu ba, a cikinta, fãce gida guda na Musulmi.
وَتَرَكْنَا فِيهَآ ءَايَةًۭ لِّلَّذِينَ يَخَافُونَ ٱلْعَذَابَ ٱلْأَلِيمَ
Kuma Muka bar wata ãyã, a cikinta, ga waɗanda ke jin tsõron azãba, mai raɗaɗi.
وَفِى مُوسَىٰٓ إِذْ أَرْسَلْنَٰهُ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ بِسُلْطَٰنٍۢ مُّبِينٍۢ
Kuma ga Mũsã, a lõkacin da Muka aiko shi zuwa ga Fir'auna da wani dalĩli bayyananne.
فَتَوَلَّىٰ بِرُكْنِهِۦ وَقَالَ سَٰحِرٌ أَوْ مَجْنُونٌۭ
Sai ya jũya bãya tãre da ƙarfinsa, kuma ya ce: "Mai sihiri ne kõ kuwa mahaukaci!"
فَأَخَذْنَٰهُ وَجُنُودَهُۥ فَنَبَذْنَٰهُمْ فِى ٱلْيَمِّ وَهُوَ مُلِيمٌۭ
Sabõda haka, Muka kama shi tãre da rundunarsa, sa'an nan Muka jẽfa su a cikin tẽku, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.
وَفِى عَادٍ إِذْ أَرْسَلْنَا عَلَيْهِمُ ٱلرِّيحَ ٱلْعَقِيمَ
Kuma ga Ãdãwa, a lõkacin da Muka aika iska ƙẽƙasasshiya a kansu.
مَا تَذَرُ مِن شَىْءٍ أَتَتْ عَلَيْهِ إِلَّا جَعَلَتْهُ كَٱلرَّمِيمِ
Bã ta barin kõme da ta jẽ a kansa, fãce ta mayar da shi kamar rududdugaggun ƙasũsuwa.
وَفِى ثَمُودَ إِذْ قِيلَ لَهُمْ تَمَتَّعُوا۟ حَتَّىٰ حِينٍۢ
Kuma ga Samũdãwa, a lõkacin da aka ce musu: "Ku ji ɗan dãɗi har wani ɗan lõkaci,"
فَعَتَوْا۟ عَنْ أَمْرِ رَبِّهِمْ فَأَخَذَتْهُمُ ٱلصَّٰعِقَةُ وَهُمْ يَنظُرُونَ
Sai suka yi girman kai ga umurnin Ubangijinsu, sabõda haka tsãwa ta kãma su, alhãli kuwa sunã kallo.
فَمَا ٱسْتَطَٰعُوا۟ مِن قِيَامٍۢ وَمَا كَانُوا۟ مُنتَصِرِينَ
Ba su kõ sãmu dãmar tsayãwa ba, kuma ba su kasance mãsu nẽman ãgaji ba.
وَقَوْمَ نُوحٍۢ مِّن قَبْلُ ۖ إِنَّهُمْ كَانُوا۟ قَوْمًۭا فَٰسِقِينَ
Da mutãnen Nũhu a gabãnin haka, lalle sun kasance waɗansu irin mutãne ne fãsiƙai.
وَٱلسَّمَآءَ بَنَيْنَٰهَا بِأَيْي۟دٍۢ وَإِنَّا لَمُوسِعُونَ
Kuma sama, mun gina ta da wani irin ƙarfi, alhãli kuwa lalle Mũ ne Mãsu yalwatãwa.
وَٱلْأَرْضَ فَرَشْنَٰهَا فَنِعْمَ ٱلْمَٰهِدُونَ
Kuma ƙasã Mun shimfiɗa ta, To, madalla da mãsu shimfiɗãwa, Mũ,
وَمِن كُلِّ شَىْءٍ خَلَقْنَا زَوْجَيْنِ لَعَلَّكُمْ تَذَكَّرُونَ
Kuma daga kõme Mun halitta nau'i biyu, watakila zã ku yi tunãni.
فَفِرُّوٓا۟ إِلَى ٱللَّهِ ۖ إِنِّى لَكُم مِّنْهُ نَذِيرٌۭ مُّبِينٌۭ
Sabõda haka ku gudu zuwa ga Allah, lalle nĩ mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.
وَلَا تَجْعَلُوا۟ مَعَ ٱللَّهِ إِلَٰهًا ءَاخَرَ ۖ إِنِّى لَكُم مِّنْهُ نَذِيرٌۭ مُّبِينٌۭ
Kuma kada ku sanya, tãre da Allah wani abin bautãwa na dabam, lalle nĩ, mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.
كَذَٰلِكَ مَآ أَتَى ٱلَّذِينَ مِن قَبْلِهِم مِّن رَّسُولٍ إِلَّا قَالُوا۟ سَاحِرٌ أَوْ مَجْنُونٌ
Kamar haka dai wani Manzo bai jẽ wa waɗanda ke gabãninsu ba fãce sun ce: "Mai sihiri ne kõ mahaukaci."
أَتَوَاصَوْا۟ بِهِۦ ۚ بَلْ هُمْ قَوْمٌۭ طَاغُونَ
shin, sunã yi wa jũna wasiyya da shi ne? Ã'a, sũ dai mutãne ne mãsu girman kai.
فَتَوَلَّ عَنْهُمْ فَمَآ أَنتَ بِمَلُومٍۢ
Sai ka jũya daga barinsu, kuma kai ba abin zargi ba ne.
وَذَكِّرْ فَإِنَّ ٱلذِّكْرَىٰ تَنفَعُ ٱلْمُؤْمِنِينَ
Kuma ka tunãtar, dõmin tunãtarwa tanã amfãnin mũminai.
وَمَا خَلَقْتُ ٱلْجِنَّ وَٱلْإِنسَ إِلَّا لِيَعْبُدُونِ
Kuma Ban halitta aljannu da mutãne ba sai dõmin su bauta Mini.
مَآ أُرِيدُ مِنْهُم مِّن رِّزْقٍۢ وَمَآ أُرِيدُ أَن يُطْعِمُونِ
Bã Ni nufln (sãmun) wani arziki daga gare su, Bã Ni nufin su (yi Mini hidimar) ciyar da Ni.
إِنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلرَّزَّاقُ ذُو ٱلْقُوَّةِ ٱلْمَتِينُ
Lalle Allah, Shĩ ne Mai azurtãwa, Mai ĩkon yi, Mai cikakken ƙarfi.
فَإِنَّ لِلَّذِينَ ظَلَمُوا۟ ذَنُوبًۭا مِّثْلَ ذَنُوبِ أَصْحَٰبِهِمْ فَلَا يَسْتَعْجِلُونِ
To, lalle waɗanda suka yi zãlunci sunã da masaki (na ɗĩban zunubi) kamar masakin abõkansu, sabõda haka kada su yi Mini gaggãwa.
فَوَيْلٌۭ لِّلَّذِينَ كَفَرُوا۟ مِن يَوْمِهِمُ ٱلَّذِى يُوعَدُونَ
Sabõda haka, bone ya tabbata ga waɗanda suka kãfirta, daga rãnar su wadda aka yi musu alkawari.
Surah 52: At-Tur — الطور
وَٱلطُّورِ
Inã rantsuwa da ¦ũr (Dũtsen Mũsã).
وَكِتَٰبٍۢ مَّسْطُورٍۢ
Da wani littãfi rubũtacce.
فِى رَقٍّۢ مَّنشُورٍۢ
A cikin wata takardar fãta shimfiɗaɗɗa.
وَٱلْبَيْتِ ٱلْمَعْمُورِ
Da Gidan da aka rãyar da shi (da ibãda).
وَٱلسَّقْفِ ٱلْمَرْفُوعِ
Da rufin nan da aka ɗaukaka.
وَٱلْبَحْرِ ٱلْمَسْجُورِ
Da tẽkun nan da aka cika (da ruwa).
إِنَّ عَذَابَ رَبِّكَ لَوَٰقِعٌۭ
Lalle, azãbar Ubangijinka, haƙĩƙa, mai aukuwa ce.
مَّا لَهُۥ مِن دَافِعٍۢ
Bã ta da mai tunkuɗẽwa.
يَوْمَ تَمُورُ ٱلسَّمَآءُ مَوْرًۭا
Rãnar da samã ke yin mõtsi tanã kai kãwo.
وَتَسِيرُ ٱلْجِبَالُ سَيْرًۭا
Kuma duwãtsu nã tafiya sunã shũɗẽwa.
فَوَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ
To, bone yã tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa.
ٱلَّذِينَ هُمْ فِى خَوْضٍۢ يَلْعَبُونَ
Waɗanda suke a cikin kududdufi sunã wãsã.
يَوْمَ يُدَعُّونَ إِلَىٰ نَارِ جَهَنَّمَ دَعًّا
Rãnar da zã a tunkuɗa su zuwa wutar Jahannama, tunkuɗãwa.
هَٰذِهِ ٱلنَّارُ ٱلَّتِى كُنتُم بِهَا تُكَذِّبُونَ
(A ce musu): "Wannan ita ce wutar da kuka kasance kunã ƙaryatãwa game da ita."
أَفَسِحْرٌ هَٰذَآ أَمْ أَنتُمْ لَا تُبْصِرُونَ
"To, shin wannan sihiri ne kõ kuwa kũ ne bã ku gani?"
ٱصْلَوْهَا فَٱصْبِرُوٓا۟ أَوْ لَا تَصْبِرُوا۟ سَوَآءٌ عَلَيْكُمْ ۖ إِنَّمَا تُجْزَوْنَ مَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَ
"Ku shigẽ ta. To, ku yi haƙuri ko kuma kada ku yi haƙuri, dai dai ne a kanku, kawai anã yi muku sakamakon abin da kuka kasance kunã aikatãwa."
إِنَّ ٱلْمُتَّقِينَ فِى جَنَّٰتٍۢ وَنَعِيمٍۢ
Lalle, mãsu taƙawa, sunã a cikin gidãjen Aljanna da wata ni'ima.
فَٰكِهِينَ بِمَآ ءَاتَىٰهُمْ رَبُّهُمْ وَوَقَىٰهُمْ رَبُّهُمْ عَذَابَ ٱلْجَحِيمِ
Sunã mãsu jin dãɗi da abin da Ubangijinsu Ya ba su, kuma Ubangijinsu Ya tsãre musu azãbar Jahĩm.
كُلُوا۟ وَٱشْرَبُوا۟ هَنِيٓـًٔۢا بِمَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَ
(A ce musu): "Ku ci, ku sha, da ni'ima, dõmin abin da kuka kasance kunã aikatãwa."
مُتَّكِـِٔينَ عَلَىٰ سُرُرٍۢ مَّصْفُوفَةٍۢ ۖ وَزَوَّجْنَٰهُم بِحُورٍ عِينٍۢ
Sunã kishingiɗe a kan karagu waɗanda ke cikin sahu, kuma Muka aurar da su waɗansu mãtã mãsu farin idãnu, mãsu girmansu.
وَٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَٱتَّبَعَتْهُمْ ذُرِّيَّتُهُم بِإِيمَٰنٍ أَلْحَقْنَا بِهِمْ ذُرِّيَّتَهُمْ وَمَآ أَلَتْنَٰهُم مِّنْ عَمَلِهِم مِّن شَىْءٍۢ ۚ كُلُّ ٱمْرِئٍۭ بِمَا كَسَبَ رَهِينٌۭ
Kuma waɗanda suka yi ĩmãni kuma zũriyarsu suka bĩ su ga ĩmãnin, Mun riskar da zũriyarsu da su, alhãli kuwa bã da Mun rage musu kõme ba daga aikinsu, kõwane mutum jingina ne ga abin da ya sana'anta.
وَأَمْدَدْنَٰهُم بِفَٰكِهَةٍۢ وَلَحْمٍۢ مِّمَّا يَشْتَهُونَ
Kuma Muka yalwata musu 'ya'yan itãce da nãma irin wanda suke marmari.
يَتَنَٰزَعُونَ فِيهَا كَأْسًۭا لَّا لَغْوٌۭ فِيهَا وَلَا تَأْثِيمٌۭ
Sunã mĩƙa wa jũnansu a cikinta hinjãlan giya, wadda bãbu yãsassar magana a cikinta, kuma bãbu jin nauyin zunubi.
۞ وَيَطُوفُ عَلَيْهِمْ غِلْمَانٌۭ لَّهُمْ كَأَنَّهُمْ لُؤْلُؤٌۭ مَّكْنُونٌۭ
Kuma waɗansu samãri nã gẽwayãwa a kansu, kamar dai sũ lu'ulu'u ne wanda ke kulle.
وَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍۢ يَتَسَآءَلُونَ
Waɗansunsu suka fuskanta zuwa ga waɗansu, sunã tambayar jũna.
قَالُوٓا۟ إِنَّا كُنَّا قَبْلُ فِىٓ أَهْلِنَا مُشْفِقِينَ
Suka ce: "Lalle mũ mun kasance a gabãnin wannan (a dũniya) a cikin iyãlanmu munã jin tsõro."
فَمَنَّ ٱللَّهُ عَلَيْنَا وَوَقَىٰنَا عَذَابَ ٱلسَّمُومِ
"To, Allah Yã yi mana kyautar falala, kuma Yã tsare mana azãbar iskar zãfi."
إِنَّا كُنَّا مِن قَبْلُ نَدْعُوهُ ۖ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلْبَرُّ ٱلرَّحِيمُ
"Lalle mũ mun kasance, a gãbanin haka, munã kiran sa. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai kyautatãwa, Mai rahama."
فَذَكِّرْ فَمَآ أَنتَ بِنِعْمَتِ رَبِّكَ بِكَاهِنٍۢ وَلَا مَجْنُونٍ
To, ka tunãtar kai fa sabõda ni'imar Ubangjinka, bã bõka kake ba, kuma bã mahaukaci ba.
أَمْ يَقُولُونَ شَاعِرٌۭ نَّتَرَبَّصُ بِهِۦ رَيْبَ ٱلْمَنُونِ
Shin zã su ce: "Mawãƙi ne, munã jiran, masĩfun mutuwa game da shĩ"?
قُلْ تَرَبَّصُوا۟ فَإِنِّى مَعَكُم مِّنَ ٱلْمُتَرَبِّصِينَ
Ka ce: "Ku yi jira, domin nĩ ma lalle inã a cikin mãsu jira tãre da ku."
أَمْ تَأْمُرُهُمْ أَحْلَٰمُهُم بِهَٰذَآ ۚ أَمْ هُمْ قَوْمٌۭ طَاغُونَ
Shin, hankulansu ne ke umarin su da wannan, kõ kuwa sũ wasu mutãne ne mãsu ƙetare haddi?
أَمْ يَقُولُونَ تَقَوَّلَهُۥ ۚ بَل لَّا يُؤْمِنُونَ
Shin, cẽwa suke yi: "Shi ne ke ƙãga faɗarsa"? Ã'a ba su dai yi ĩmãni ba.
فَلْيَأْتُوا۟ بِحَدِيثٍۢ مِّثْلِهِۦٓ إِن كَانُوا۟ صَٰدِقِينَ
Sai su zõ da wani lãbãri mai misãlinsa idan sun kasance sũmãsu gaskiya ne.
أَمْ خُلِقُوا۟ مِنْ غَيْرِ شَىْءٍ أَمْ هُمُ ٱلْخَٰلِقُونَ
Shin, an halitta su ne bã daga kõme ba, kõ kuwa sũ ne mãsu yin halitta?
أَمْ خَلَقُوا۟ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضَ ۚ بَل لَّا يُوقِنُونَ
Shin, sun halitta sammai da ƙasa ne? Ã'a ba su dai yi ĩmãnin yaƙĩni ba.
أَمْ عِندَهُمْ خَزَآئِنُ رَبِّكَ أَمْ هُمُ ٱلْمُصَۣيْطِرُونَ
Shin, taskõkin Ubangijinka, sunã a wurinsu ne? Kõ kuwa sũ ne mãsu rinjãya?
أَمْ لَهُمْ سُلَّمٌۭ يَسْتَمِعُونَ فِيهِ ۖ فَلْيَأْتِ مُسْتَمِعُهُم بِسُلْطَٰنٍۢ مُّبِينٍ
Shin, sunã da wani tsãni ne wanda suke (hawa sunã) saurãron (lãbãrin samã) a cikinsa? Sai mai saurarõnsu ya zo da wani dalĩli bayyananne.
أَمْ لَهُ ٱلْبَنَٰتُ وَلَكُمُ ٱلْبَنُونَ
Shin, Yanã da 'ya'ya mãtã ne kuma kũ, kunã da ɗiya maza ne?
أَمْ تَسْـَٔلُهُمْ أَجْرًۭا فَهُم مِّن مَّغْرَمٍۢ مُّثْقَلُونَ
Shin, kanã tambayar su wata ijãra ne, sabõda haka suka zama mãsu jin nauyin biyan tãrar?
أَمْ عِندَهُمُ ٱلْغَيْبُ فَهُمْ يَكْتُبُونَ
Shin, a wurinsu akwai ilmin gaibi, sabõda haka sunã rubũtãwa?
أَمْ يُرِيدُونَ كَيْدًۭا ۖ فَٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ هُمُ ٱلْمَكِيدُونَ
Shin, sunã nufin wani kaidi ne? To, waɗanda suka kãfirta sũ ne waɗanda ake yi wa kaidi.
أَمْ لَهُمْ إِلَٰهٌ غَيْرُ ٱللَّهِ ۚ سُبْحَٰنَ ٱللَّهِ عَمَّا يُشْرِكُونَ
Shin, sunã da wani abin bautãwa ne wanda bã Allah ba? Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke yi na shirki!
وَإِن يَرَوْا۟ كِسْفًۭا مِّنَ ٱلسَّمَآءِ سَاقِطًۭا يَقُولُوا۟ سَحَابٌۭ مَّرْكُومٌۭ
Kuma idan sun ga wani ɓaɓɓake daga samã yãnã fãɗuwa, sai su ce wani girgije ne, mai hauhawar jũna.
فَذَرْهُمْ حَتَّىٰ يُلَٰقُوا۟ يَوْمَهُمُ ٱلَّذِى فِيهِ يُصْعَقُونَ
To, ka bar su, sai sun haɗu da yinin nan da za a sũmar da su a cikinsa.
يَوْمَ لَا يُغْنِى عَنْهُمْ كَيْدُهُمْ شَيْـًۭٔا وَلَا هُمْ يُنصَرُونَ
Rãnar da kaidinsu bã ya wadãtar masu da kõme, kuma bã a taimakon su.
وَإِنَّ لِلَّذِينَ ظَلَمُوا۟ عَذَابًۭا دُونَ ذَٰلِكَ وَلَٰكِنَّ أَكْثَرَهُمْ لَا يَعْلَمُونَ
Kuma lalle, waɗannan da suka yi zãluncin, sunã da azãba (a nan dũniya) banda waccan, kuma mafi yawansu ba su sani ba.
وَٱصْبِرْ لِحُكْمِ رَبِّكَ فَإِنَّكَ بِأَعْيُنِنَا ۖ وَسَبِّحْ بِحَمْدِ رَبِّكَ حِينَ تَقُومُ
Sai ka yi hakuri da hukuncin Ubangijinka, lalle kai fa kanã idãnunMu, kuma ka tsarkake Ubangijinka da (tasbĩhi) game da gõde Masa a lõkacin da kake tãshi tsaye (dõmin salla kõ wani abu).
وَمِنَ ٱلَّيْلِ فَسَبِّحْهُ وَإِدْبَٰرَ ٱلنُّجُومِ
Kuma daga dare, sai ka tsarkake Shi (da tasbĩhin) dalõkacin jũyãwar taurãri.
Surah 53: An-Najm — النجم
وَٱلنَّجْمِ إِذَا هَوَىٰ
Inã rantsuwa da taurãron, a lõkacin da ya faku.
مَا ضَلَّ صَاحِبُكُمْ وَمَا غَوَىٰ
Ma'abũcinku bai ɓata ba, kuma bai ƙẽtare haddi ba.
وَمَا يَنطِقُ عَنِ ٱلْهَوَىٰٓ
Kuma bã ya yin magana daga son zuciyarsa.
إِنْ هُوَ إِلَّا وَحْىٌۭ يُوحَىٰ
(Maganarsa) ba ta zamo ba, fãce wahayi ne da ake aikõwa.
عَلَّمَهُۥ شَدِيدُ ٱلْقُوَىٰ
(Malã'ika) mai tsananin ƙarfi ya sanar da shi.
ذُو مِرَّةٍۢ فَٱسْتَوَىٰ
Ma'abũcin ƙarfi da kwarjini, sa'an nan ya daidaita.
وَهُوَ بِٱلْأُفُقِ ٱلْأَعْلَىٰ
Alhãli kuwa yanã a sararin samã mafi aukaka.
ثُمَّ دَنَا فَتَدَلَّىٰ
Sa'an nan ya kusanta, kuma ya matsa zurõwa.
فَكَانَ قَابَ قَوْسَيْنِ أَوْ أَدْنَىٰ
Har ya kasance gwargwadon zirã'i biyu, kõ kuma abin da ya fi kusa.
فَأَوْحَىٰٓ إِلَىٰ عَبْدِهِۦ مَآ أَوْحَىٰ
Sa'an nan ya yi wahayi zuwa ga bãwan Allah (Muhammadu) da abin da ya faɗa (masa).
مَا كَذَبَ ٱلْفُؤَادُ مَا رَأَىٰٓ
Zũciyar (Annabi) bata ƙaryata abin da ya gani ba.
أَفَتُمَٰرُونَهُۥ عَلَىٰ مَا يَرَىٰ
Shin, zã ku yi masa musu a kan abin da yake gani?
وَلَقَدْ رَءَاهُ نَزْلَةً أُخْرَىٰ
Kuma lalle ya gan shi, haƙĩƙatan, a wani lõkacin saukarsa.
عِندَ سِدْرَةِ ٱلْمُنتَهَىٰ
A wurin da magaryar tuƙẽwa take.
عِندَهَا جَنَّةُ ٱلْمَأْوَىٰٓ
A inda taken, nan Aljannar makoma take.
إِذْ يَغْشَى ٱلسِّدْرَةَ مَا يَغْشَىٰ
Lõkacin da abin da yake rufe magaryar tuƙẽwa ya rufe ta.
مَا زَاغَ ٱلْبَصَرُ وَمَا طَغَىٰ
Ganinsa bai karkata ba, kuma bai ƙetare haddi ba.
لَقَدْ رَأَىٰ مِنْ ءَايَٰتِ رَبِّهِ ٱلْكُبْرَىٰٓ
Lalle, tabbas, (Annabinku) ya ga waɗanda suka fi girma daga ãyõyin Ubangijinsa.
أَفَرَءَيْتُمُ ٱللَّٰتَ وَٱلْعُزَّىٰ
Shin, kun ga Lãta da uzza?
وَمَنَوٰةَ ٱلثَّالِثَةَ ٱلْأُخْرَىٰٓ
Da (wani gunki wai shi) Manãta, na ukunsu?
أَلَكُمُ ٱلذَّكَرُ وَلَهُ ٱلْأُنثَىٰ
Ashe, kũ ne da ɗa namiji Shĩ (Allah) kuma da ɗiya mace?
تِلْكَ إِذًۭا قِسْمَةٌۭ ضِيزَىٰٓ
Wannan fa ya zama rabo naƙasasshe.
إِنْ هِىَ إِلَّآ أَسْمَآءٌۭ سَمَّيْتُمُوهَآ أَنتُمْ وَءَابَآؤُكُم مَّآ أَنزَلَ ٱللَّهُ بِهَا مِن سُلْطَٰنٍ ۚ إِن يَتَّبِعُونَ إِلَّا ٱلظَّنَّ وَمَا تَهْوَى ٱلْأَنفُسُ ۖ وَلَقَدْ جَآءَهُم مِّن رَّبِّهِمُ ٱلْهُدَىٰٓ
Waɗannan bã kõme ba ne fãce sũnãye, waɗanda kuka ambace su da su, kũ da uwãyenku. Allah bai saukar da wani dalĩli game da su ba. (Kãfirai) bã su biyar kõme fãce zato da abin da rãyukansu ke so, Alhãli kuwa shiriyar ta daga wajen Ubangijinsu, ta jẽ musu (sai suka bar ta suka kõma wa zaton).
أَمْ لِلْإِنسَٰنِ مَا تَمَنَّىٰ
Ko (an fai cẽwa) mutum zai sãmi abin da yake gũri?
فَلِلَّهِ ٱلْءَاخِرَةُ وَٱلْأُولَىٰ
To, Lãhira da dũniya na Allah kawai ne (wanda ya nẽme su daga wani, yã yi kuskure).
۞ وَكَم مِّن مَّلَكٍۢ فِى ٱلسَّمَٰوَٰتِ لَا تُغْنِى شَفَٰعَتُهُمْ شَيْـًٔا إِلَّا مِنۢ بَعْدِ أَن يَأْذَنَ ٱللَّهُ لِمَن يَشَآءُ وَيَرْضَىٰٓ
Akwai malã'iku da yawa a cikin sammai cẽtonsu bã ya wadãtar da kõme fãce bãyan Allah Yã yi izni (da shi) ga wanda Yake so, kuma Yake yarda.
إِنَّ ٱلَّذِينَ لَا يُؤْمِنُونَ بِٱلْءَاخِرَةِ لَيُسَمُّونَ ٱلْمَلَٰٓئِكَةَ تَسْمِيَةَ ٱلْأُنثَىٰ
Lalle waɗannan da bã su yin ĩmãni da Lãhira, haƙĩƙa sunã kiran malã'iku da sũnan mace.
وَمَا لَهُم بِهِۦ مِنْ عِلْمٍ ۖ إِن يَتَّبِعُونَ إِلَّا ٱلظَّنَّ ۖ وَإِنَّ ٱلظَّنَّ لَا يُغْنِى مِنَ ٱلْحَقِّ شَيْـًۭٔا
Kuma bã su da wani ilmi game da shi, bã su bin kõme fãce zato alhãli kuwa lalle zato bã ya amfãnar da kõme daga gaskiya.
فَأَعْرِضْ عَن مَّن تَوَلَّىٰ عَن ذِكْرِنَا وَلَمْ يُرِدْ إِلَّا ٱلْحَيَوٰةَ ٱلدُّنْيَا
Sabõda haka sai ka kau da kai daga wanda ya jũya bãya daga ambatonMu kuma bai yi nufin kõme ba fãce rãyuwar kusa (dũniya).
ذَٰلِكَ مَبْلَغُهُم مِّنَ ٱلْعِلْمِ ۚ إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعْلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِۦ وَهُوَ أَعْلَمُ بِمَنِ ٱهْتَدَىٰ
Wannan ita ce iyãkar abin da suke iya kai gare shi na ilmi. lalle Ubangijinka Shĩ ne Mafi sanin wanda ya ɓace daga hanyarSa, kuma Shi ne Mafi sani ga wanda ya nẽmi shiriya.
وَلِلَّهِ مَا فِى ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِى ٱلْأَرْضِ لِيَجْزِىَ ٱلَّذِينَ أَسَٰٓـُٔوا۟ بِمَا عَمِلُوا۟ وَيَجْزِىَ ٱلَّذِينَ أَحْسَنُوا۟ بِٱلْحُسْنَى
Kuma abin da ke cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasã na Allah kawai ne, dõmin Yã sãka wa waɗanda suka mũnana da abin da suka aikata, kuma Ya sãka wa waɗanda suki kyautata da sakamakon da ya fi kyau.
ٱلَّذِينَ يَجْتَنِبُونَ كَبَٰٓئِرَ ٱلْإِثْمِ وَٱلْفَوَٰحِشَ إِلَّا ٱللَّمَمَ ۚ إِنَّ رَبَّكَ وَٰسِعُ ٱلْمَغْفِرَةِ ۚ هُوَ أَعْلَمُ بِكُمْ إِذْ أَنشَأَكُم مِّنَ ٱلْأَرْضِ وَإِذْ أَنتُمْ أَجِنَّةٌۭ فِى بُطُونِ أُمَّهَٰتِكُمْ ۖ فَلَا تُزَكُّوٓا۟ أَنفُسَكُمْ ۖ هُوَ أَعْلَمُ بِمَنِ ٱتَّقَىٰٓ
Waɗanda ke nĩsantar manyan zunubai da abũbuwan alfãsha, fãce ƙanãnan laifuffuka, lalle Ubangijinka Mai yalwatattar gãfara ne, Shĩ ne Ya fi sani ga abinda ke gare ku a lõkacin da Ya ƙãga halittarku daga ƙasa, kuma a lõkacin da kuke tãyuna a cikin cikannan uwãyenku. Sabõda haka, kada ku tsarkake kanku, Shĩ ne Mafi sani ga wanda ya yi taƙawa.
أَفَرَءَيْتَ ٱلَّذِى تَوَلَّىٰ
Shin, ka ga wannan da ya jũya baya?
وَأَعْطَىٰ قَلِيلًۭا وَأَكْدَىٰٓ
Ya yi kyauta kaɗan, kuma ya yi rowa?
أَعِندَهُۥ عِلْمُ ٱلْغَيْبِ فَهُوَ يَرَىٰٓ
Shin, akwai ilmin gaibi a wurinsa, Sabõda haka yanã ganin gaibin?
أَمْ لَمْ يُنَبَّأْ بِمَا فِى صُحُفِ مُوسَىٰ
Ko kuwa ba a ba shi lãbãri ba ga abin da yake a cikin Littafan Mũsã?
وَإِبْرَٰهِيمَ ٱلَّذِى وَفَّىٰٓ
Da Ibrãhĩm wanda ya cika alkawari?
أَلَّا تَزِرُ وَازِرَةٌۭ وِزْرَ أُخْرَىٰ
Cẽwa wani rai mai kãyan laifi bã ya ɗaukar kãyan laifin wani.
وَأَن لَّيْسَ لِلْإِنسَٰنِ إِلَّا مَا سَعَىٰ
Kuma mutum bã shi da kõme fãce abin da ya aikata.
وَأَنَّ سَعْيَهُۥ سَوْفَ يُرَىٰ
Kuma lalle, aikinsa zã a gan shi.
ثُمَّ يُجْزَىٰهُ ٱلْجَزَآءَ ٱلْأَوْفَىٰ
Sa'an nan a sãka masa da sakamako wanda yake mafi cikar ma'auni?
وَأَنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ ٱلْمُنتَهَىٰ
Kuma lalle, makõmar zuwa Ubangijinka kawai take?
وَأَنَّهُۥ هُوَ أَضْحَكَ وَأَبْكَىٰ
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya sanya dariya, kuma Ya sanya kũka.
وَأَنَّهُۥ هُوَ أَمَاتَ وَأَحْيَا
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya kashe, kuma Ya rãyar.
وَأَنَّهُۥ خَلَقَ ٱلزَّوْجَيْنِ ٱلذَّكَرَ وَٱلْأُنثَىٰ
Kuma lalle Shĩ ne Ya yi halitta nau'i-nau'i, namiji da mace.
مِن نُّطْفَةٍ إِذَا تُمْنَىٰ
Daga wani ɗigon ruwa guda a lõkacin da ake jẽfa shi a cikin mahaifa.
وَأَنَّ عَلَيْهِ ٱلنَّشْأَةَ ٱلْأُخْرَىٰ
Kuma a kansa ne ƙãga halitta ta biyu take.
وَأَنَّهُۥ هُوَ أَغْنَىٰ وَأَقْنَىٰ
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya azurta, kuma Ya wadãtar.
وَأَنَّهُۥ هُوَ رَبُّ ٱلشِّعْرَىٰ
Kuma lalle, Shĩ, Shi ne Ubangijin Shi'ira.
وَأَنَّهُۥٓ أَهْلَكَ عَادًا ٱلْأُولَىٰ
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya halaka Ãdãwa na farko.
وَثَمُودَا۟ فَمَآ أَبْقَىٰ
Da Samũdãwa, sa'an nan bai rage su ba.
وَقَوْمَ نُوحٍۢ مِّن قَبْلُ ۖ إِنَّهُمْ كَانُوا۟ هُمْ أَظْلَمَ وَأَطْغَىٰ
Da mutãnen Nũhu a gabãnin haka, lalle sũ sun kasance mafi zãlunci kuma mafi girman kai.
وَٱلْمُؤْتَفِكَةَ أَهْوَىٰ
Da waɗanda aka birkice ƙasarsu, Ya kãyar da su.
فَغَشَّىٰهَا مَا غَشَّىٰ
Sa'an nan abin da ya rufe su, ya rufe su.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكَ تَتَمَارَىٰ
To, da wace daga ni'imõmin Ubangijinka kake yin shakka?
هَٰذَا نَذِيرٌۭ مِّنَ ٱلنُّذُرِ ٱلْأُولَىٰٓ
wannan (Muhammadu) mai gargaɗi ne kamar irin mãsu gargaɗi na farko.
أَزِفَتِ ٱلْءَازِفَةُ
Makusanciya fa, tã yi kusa.
لَيْسَ لَهَا مِن دُونِ ٱللَّهِ كَاشِفَةٌ
Bãbu wani rai, banda Allah, mai iya bãyani gare ta.
أَفَمِنْ هَٰذَا ٱلْحَدِيثِ تَعْجَبُونَ
Shin, kuma daga wannan lãbãri kuke mãmãki?
وَتَضْحَكُونَ وَلَا تَبْكُونَ
Kuma kunã yin dãriya, kuma bã ku yin kũka?
وَأَنتُمْ سَٰمِدُونَ
Alhãli kunã mãsu wãsã?
فَٱسْجُدُوا۟ لِلَّهِ وَٱعْبُدُوا۟ ۩
To, ku yi tawãli'u ga Allah, kuma ku bauta (masa).
Surah 54: Al-Qamar — القمر
ٱقْتَرَبَتِ ٱلسَّاعَةُ وَٱنشَقَّ ٱلْقَمَرُ
Sã'a ta yi kusa, kuma wata ya tsãge.
وَإِن يَرَوْا۟ ءَايَةًۭ يُعْرِضُوا۟ وَيَقُولُوا۟ سِحْرٌۭ مُّسْتَمِرٌّۭ
Kuma idan sun ga wata ãyã, sai su juya baya su ce: "Sihiri ne mai dõgẽwa!"
وَكَذَّبُوا۟ وَٱتَّبَعُوٓا۟ أَهْوَآءَهُمْ ۚ وَكُلُّ أَمْرٍۢ مُّسْتَقِرٌّۭ
Kuma suka ƙaryata, kuma suka bi son zũciyarsu, alhãli kuwa kõwane al'amari (wanda suke son su tũre daga Annabi) an tabbatar da shi.
وَلَقَدْ جَآءَهُم مِّنَ ٱلْأَنۢبَآءِ مَا فِيهِ مُزْدَجَرٌ
Kuma lalle, abin da yake akwai tsãwatarwa a cikinsa na lãbãraiya zo musu.
حِكْمَةٌۢ بَٰلِغَةٌۭ ۖ فَمَا تُغْنِ ٱلنُّذُرُ
Hikima cikakka! Sai dai abũbuwan gargaɗi bã su amfãni.
فَتَوَلَّ عَنْهُمْ ۘ يَوْمَ يَدْعُ ٱلدَّاعِ إِلَىٰ شَىْءٍۢ نُّكُرٍ
Sabõda haka, ka bar su! Rãnar da mai kiran zai yi kira zuwa ga wani abu abin ƙyama.
خُشَّعًا أَبْصَٰرُهُمْ يَخْرُجُونَ مِنَ ٱلْأَجْدَاثِ كَأَنَّهُمْ جَرَادٌۭ مُّنتَشِرٌۭ
¡asƙantattu ga idanunsu zã su fito daga kaburburansu, kamar dai sũ fãri ne waɗandasuka wãtse.
مُّهْطِعِينَ إِلَى ٱلدَّاعِ ۖ يَقُولُ ٱلْكَٰفِرُونَ هَٰذَا يَوْمٌ عَسِرٌۭ
Sunã gaggãwar tafiya zuwa ga mai kiran, kãfirai na cẽwa, "Wannan yini ne mai wuya!"
۞ كَذَّبَتْ قَبْلَهُمْ قَوْمُ نُوحٍۢ فَكَذَّبُوا۟ عَبْدَنَا وَقَالُوا۟ مَجْنُونٌۭ وَٱزْدُجِرَ
Mutãnen Nũhu sun ƙaryata, a gabãninsu, sai suka ƙaryata BawanMu, kuma suka ce: "Shi mahaukaci ne." Kuma aka tsãwace shi.
فَدَعَا رَبَّهُۥٓ أَنِّى مَغْلُوبٌۭ فَٱنتَصِرْ
Sabõda haka, ya kira Ubangijinsa (ya ce), "Lalle nĩ, an rinjãye ni, sai Ka yi taimako."
فَفَتَحْنَآ أَبْوَٰبَ ٱلسَّمَآءِ بِمَآءٍۢ مُّنْهَمِرٍۢ
Sai Muka bũɗe kõfõfin sama da ruwa mai zuba.
وَفَجَّرْنَا ٱلْأَرْضَ عُيُونًۭا فَٱلْتَقَى ٱلْمَآءُ عَلَىٰٓ أَمْرٍۢ قَدْ قُدِرَ
Kuma Muka ɓuɓɓugar da ƙasã ta zama idãnun ruwa, daɗa ruwa ya haɗu a kan wani umurni da aka riga aka ƙaddara shi.
وَحَمَلْنَٰهُ عَلَىٰ ذَاتِ أَلْوَٰحٍۢ وَدُسُرٍۢ
Kuma Muka ɗauke Nũhu a kan (jirgi) na alluna da ƙũsõshi.
تَجْرِى بِأَعْيُنِنَا جَزَآءًۭ لِّمَن كَانَ كُفِرَ
Tanã gudãna, a kan idãnunMu, dõmin sakamako ga wanda aka yi wa kãfircin.
وَلَقَد تَّرَكْنَٰهَآ ءَايَةًۭ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍۢ
Kuma lalle, Mun bar ta ta zama ãyã. To, Shin, akwai mai tunãni
فَكَيْفَ كَانَ عَذَابِى وَنُذُرِ
To, yãyã azãbãTa take da gargaɗiNa?
وَلَقَدْ يَسَّرْنَا ٱلْقُرْءَانَ لِلذِّكْرِ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍۢ
Kuma lalle ne, haƙĩkƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur'ãni, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?
كَذَّبَتْ عَادٌۭ فَكَيْفَ كَانَ عَذَابِى وَنُذُرِ
Ãdãwa sun ƙaryata, to, yãya azãbãTa take, da gargaɗiNa?
إِنَّآ أَرْسَلْنَا عَلَيْهِمْ رِيحًۭا صَرْصَرًۭا فِى يَوْمِ نَحْسٍۢ مُّسْتَمِرٍّۢ
Lalle Mũ, Mun aika da iska mai tsananin sauti a kansu, a cikin wani yinin nahĩsa mai dõgẽwa.
تَنزِعُ ٱلنَّاسَ كَأَنَّهُمْ أَعْجَازُ نَخْلٍۢ مُّنقَعِرٍۢ
Tanã fizgar mutãne kamar dai sũ kututturan dabĩno tumɓukakku ne.
فَكَيْفَ كَانَ عَذَابِى وَنُذُرِ
To, yãya azãbãTa take da gargaɗiNa?
وَلَقَدْ يَسَّرْنَا ٱلْقُرْءَانَ لِلذِّكْرِ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍۢ
Kuma lalle ne, haƙiƙa Mun sauƙaƙe Alƙur'ani, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?
كَذَّبَتْ ثَمُودُ بِٱلنُّذُرِ
Samũdãwa sun ƙaryata game da gargaɗin.
فَقَالُوٓا۟ أَبَشَرًۭا مِّنَّا وَٰحِدًۭا نَّتَّبِعُهُۥٓ إِنَّآ إِذًۭا لَّفِى ضَلَٰلٍۢ وَسُعُرٍ
Sai suka ce: "Wani mutum daga cikinmu, shi kaɗai, wai mu bĩ shi! Lalle mũ a lõkacin, haƙĩƙa mun shiga wata ɓata da haukã.
أَءُلْقِىَ ٱلذِّكْرُ عَلَيْهِ مِنۢ بَيْنِنَا بَلْ هُوَ كَذَّابٌ أَشِرٌۭ
"Shin, an jẽfa masa Manzancin ne, a tsakãninmu? Ã'a, shĩ dai gawurtaccen maƙaryaci ne mai girman kai!"
سَيَعْلَمُونَ غَدًۭا مَّنِ ٱلْكَذَّابُ ٱلْأَشِرُ
Zã su sani a gõbe, wãne ne gawurtaccen mai ƙaryar, mai girman kan?
إِنَّا مُرْسِلُوا۟ ٱلنَّاقَةِ فِتْنَةًۭ لَّهُمْ فَٱرْتَقِبْهُمْ وَٱصْطَبِرْ
Lalle Mũ, mãsu aikãwa da rãƙumar ne, ta zame musu fitina, sai ka tsare su da kallo, kuma ka yi haƙuri.
وَنَبِّئْهُمْ أَنَّ ٱلْمَآءَ قِسْمَةٌۢ بَيْنَهُمْ ۖ كُلُّ شِرْبٍۢ مُّحْتَضَرٌۭ
Kuma ka bã su lãbãri cẽwa ruwa rababbe ne a tsakãninsu (da rãƙumar), kõwane sha, mai shi yanã halartar sa.
فَنَادَوْا۟ صَاحِبَهُمْ فَتَعَاطَىٰ فَعَقَرَ
Sai suka kira abokinsu, sai ya karɓa, sa'an nan ya sõke ta,
فَكَيْفَ كَانَ عَذَابِى وَنُذُرِ
To, yãya azãbaTa take da gargaɗiNa?
إِنَّآ أَرْسَلْنَا عَلَيْهِمْ صَيْحَةًۭ وَٰحِدَةًۭ فَكَانُوا۟ كَهَشِيمِ ٱلْمُحْتَظِرِ
Lalle Mũ, Mun aika tsãwa guda a kansu, sai suka kasance kamar yãyin mai shinge.
وَلَقَدْ يَسَّرْنَا ٱلْقُرْءَانَ لِلذِّكْرِ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍۢ
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur'ani, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?
كَذَّبَتْ قَوْمُ لُوطٍۭ بِٱلنُّذُرِ
Mutãnen Lũɗu sun ƙaryata, game da gargaɗi.
إِنَّآ أَرْسَلْنَا عَلَيْهِمْ حَاصِبًا إِلَّآ ءَالَ لُوطٍۢ ۖ نَّجَّيْنَٰهُم بِسَحَرٍۢ
Lalle Mun aika iskar tsakuwa a kansu, fãce mabiyan Lũɗu, Mun tsirar da su a lõkacin asuba.
نِّعْمَةًۭ مِّنْ عِندِنَا ۚ كَذَٰلِكَ نَجْزِى مَن شَكَرَ
Sabõda wata ni'ima ta daga gare Mu. Kamar haka Muke sãka wa wanda ya gõde.
وَلَقَدْ أَنذَرَهُم بَطْشَتَنَا فَتَمَارَوْا۟ بِٱلنُّذُرِ
Kuma lalle, haƙĩƙa, ya yi musu gargaɗin damƙarMu, sai suka yi musu game da gargaɗin.
وَلَقَدْ رَٰوَدُوهُ عَن ضَيْفِهِۦ فَطَمَسْنَآ أَعْيُنَهُمْ فَذُوقُوا۟ عَذَابِى وَنُذُرِ
Kuma lalle haƙĩƙa, su, sun nẽme shi ta wajen bãƙinsa, sai Muka shãfe idãnunsu. "To, ku ɗanɗani azãbaTa da gargaɗĩNa."
وَلَقَدْ صَبَّحَهُم بُكْرَةً عَذَابٌۭ مُّسْتَقِرٌّۭ
Kuma lalle, haƙĩƙa, wata azãba matabbaciya tã wãye musu gari da yãƙi, tun da sãfe.
فَذُوقُوا۟ عَذَابِى وَنُذُرِ
To, ku ɗanɗani azãbãTa da gargaɗĩNa.
وَلَقَدْ يَسَّرْنَا ٱلْقُرْءَانَ لِلذِّكْرِ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍۢ
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur, ani dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?
وَلَقَدْ جَآءَ ءَالَ فِرْعَوْنَ ٱلنُّذُرُ
Kuma lalle, haƙĩƙa, gargaɗin ya jẽ wa mabiyan Fir'auna.
كَذَّبُوا۟ بِـَٔايَٰتِنَا كُلِّهَا فَأَخَذْنَٰهُمْ أَخْذَ عَزِيزٍۢ مُّقْتَدِرٍ
Sun ƙaryata game da ãyõyinMu, dukansu sai Muka kãma su, irin kãmun Mabuwãyi, Mai ĩkon yi.
أَكُفَّارُكُمْ خَيْرٌۭ مِّنْ أُو۟لَٰٓئِكُمْ أَمْ لَكُم بَرَآءَةٌۭ فِى ٱلزُّبُرِ
Shin, kãfiranku ne mafi alhẽri daga waɗancan, ko kuwa kunã da wata barã'a a cikin littattafai?
أَمْ يَقُولُونَ نَحْنُ جَمِيعٌۭ مُّنتَصِرٌۭ
Kõ zã su ce: "Mũ duka mãsu haɗa ƙarfi ne dõmin cin nasara?"
سَيُهْزَمُ ٱلْجَمْعُ وَيُوَلُّونَ ٱلدُّبُرَ
Zã a karya tãron, kuma su jũya bãya dõmin gudu.
بَلِ ٱلسَّاعَةُ مَوْعِدُهُمْ وَٱلسَّاعَةُ أَدْهَىٰ وَأَمَرُّ
Ã'a, Sã'a ita cẽ lõkacin wa'adinsu, kuma Sã'ar tã fi tsananin masĩfa, kuma ta fiɗãci.
إِنَّ ٱلْمُجْرِمِينَ فِى ضَلَٰلٍۢ وَسُعُرٍۢ
Lalle ne, mãsu laifi sunã a cikin ɓata da hauka.
يَوْمَ يُسْحَبُونَ فِى ٱلنَّارِ عَلَىٰ وُجُوهِهِمْ ذُوقُوا۟ مَسَّ سَقَرَ
Rãnar da zã a jã su a cikin wuta a kan fuskõkinsu. "Ku ɗanɗani shãfar wutar Saƙar."
إِنَّا كُلَّ شَىْءٍ خَلَقْنَٰهُ بِقَدَرٍۢ
Lalle Mũ, kõwane irin abu Mun halitta shi a kan tsãri.
وَمَآ أَمْرُنَآ إِلَّا وَٰحِدَةٌۭ كَلَمْحٍۭ بِٱلْبَصَرِ
Kuma umurninMu bai zamo ba fãce da kalma ɗaya, kamar walƙãwar ido.
وَلَقَدْ أَهْلَكْنَآ أَشْيَاعَكُمْ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍۢ
Kuma lalle ne haƙĩƙa, Mun halaka irin gayyarku. To, shin, akwai mai tunãni?
وَكُلُّ شَىْءٍۢ فَعَلُوهُ فِى ٱلزُّبُرِ
Kuma kõwane abu, da suka aikata shi, yanã a cikin littattafai.
وَكُلُّ صَغِيرٍۢ وَكَبِيرٍۢ مُّسْتَطَرٌ
Kuma dukkan ƙarami da babba, rubutacce ne.
إِنَّ ٱلْمُتَّقِينَ فِى جَنَّٰتٍۢ وَنَهَرٍۢ
Lalle mãsu taƙawa sunã a cikin gidãjen Aljanna da kõguna.
فِى مَقْعَدِ صِدْقٍ عِندَ مَلِيكٍۢ مُّقْتَدِرٍۭ
A cikin mazaunin gaskiya, wurin Mai ikon yi, Mai iya zartaswa.
Surah 55: Ar-Rahman — الرحمن
ٱلرَّحْمَٰنُ
(Allah) Mai rahama.
عَلَّمَ ٱلْقُرْءَانَ
Yã sanar da Alƙur'ani.
خَلَقَ ٱلْإِنسَٰنَ
Yã halitta mutum.
عَلَّمَهُ ٱلْبَيَانَ
Yã sanar da shi bayãni (magana).
ٱلشَّمْسُ وَٱلْقَمَرُ بِحُسْبَانٍۢ
Rãnã da watã a kan lissãfi suke.
وَٱلنَّجْمُ وَٱلشَّجَرُ يَسْجُدَانِ
Kuma tsirrai mãsu yãɗo da itãce sunã tawãlu'i.
وَٱلسَّمَآءَ رَفَعَهَا وَوَضَعَ ٱلْمِيزَانَ
Kuma samã Ya ɗaukaka ta, Kuma Yã aza sikẽli.
أَلَّا تَطْغَوْا۟ فِى ٱلْمِيزَانِ
Dõmin kada ku karkatar da sikẽlin.
وَأَقِيمُوا۟ ٱلْوَزْنَ بِٱلْقِسْطِ وَلَا تُخْسِرُوا۟ ٱلْمِيزَانَ
Kuma ku daidaita awo da ãdalci, kuma kada ku rage sikẽlin.
وَٱلْأَرْضَ وَضَعَهَا لِلْأَنَامِ
Kuma ƙasã Yã aza ta dõmin tãlikai.
فِيهَا فَٰكِهَةٌۭ وَٱلنَّخْلُ ذَاتُ ٱلْأَكْمَامِ
A cikinta akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno mai kwasfa.
وَٱلْحَبُّ ذُو ٱلْعَصْفِ وَٱلرَّيْحَانُ
Da ƙwãya mai sõshiya da ƙamshi.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangjinku kuke ƙaryatãwa?
خَلَقَ ٱلْإِنسَٰنَ مِن صَلْصَٰلٍۢ كَٱلْفَخَّارِ
Yã halitta mutum daga ƙẽkasasshen yumɓu kumar kasko.
وَخَلَقَ ٱلْجَآنَّ مِن مَّارِجٍۢ مِّن نَّارٍۢ
Kuma ya halitta aljani daga bira daga wutã.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
رَبُّ ٱلْمَشْرِقَيْنِ وَرَبُّ ٱلْمَغْرِبَيْنِ
Ubangjin mafita biyu na rãnã, kuma Ubangijin mafãɗã biyu na rãnã.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
مَرَجَ ٱلْبَحْرَيْنِ يَلْتَقِيَانِ
Yã garwaya tẽku biyu (ruwan dãɗi da na zartsi) sunã haɗuwa.
بَيْنَهُمَا بَرْزَخٌۭ لَّا يَبْغِيَانِ
A tsakãninsu akwai shãmaki, bã za su ƙetare haddi ba.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
يَخْرُجُ مِنْهُمَا ٱللُّؤْلُؤُ وَٱلْمَرْجَانُ
Lu'ulu'u da murjãni na fita daga gare su.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
وَلَهُ ٱلْجَوَارِ ٱلْمُنشَـَٔاتُ فِى ٱلْبَحْرِ كَٱلْأَعْلَٰمِ
Kuma Yanã da manyan jirãge, waɗanda ake ƙãgãwa a cikin tẽku kamar manyan duwãtsu.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
كُلُّ مَنْ عَلَيْهَا فَانٍۢ
Dukkan wanda ke kanta mai ƙãrẽwa ne.
وَيَبْقَىٰ وَجْهُ رَبِّكَ ذُو ٱلْجَلَٰلِ وَٱلْإِكْرَامِ
Kuma Fuskarar Ubangijinka, Mai girman Jalala da karimci, ita ce take wanzuwa.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
يَسْـَٔلُهُۥ مَن فِى ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ ۚ كُلَّ يَوْمٍ هُوَ فِى شَأْنٍۢ
wanda ke a cikin sammai da ƙasã yanã rõƙon Sa (Allah), a kullum Allah na a cikin wani sha'ani.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
سَنَفْرُغُ لَكُمْ أَيُّهَ ٱلثَّقَلَانِ
Zã mu ɗauki lõkaci sabõda ku, yã kũ mãsu nauyin halitta biyu!
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
يَٰمَعْشَرَ ٱلْجِنِّ وَٱلْإِنسِ إِنِ ٱسْتَطَعْتُمْ أَن تَنفُذُوا۟ مِنْ أَقْطَارِ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ فَٱنفُذُوا۟ ۚ لَا تَنفُذُونَ إِلَّا بِسُلْطَٰنٍۢ
Ya jama'ar aljannu da mutãne! Idan kunã iya zarcẽwa daga sãsannin sammai da ƙasã to ku zarce. Bã za ku iya zarcẽwaba fãce da wani dalĩli.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
يُرْسَلُ عَلَيْكُمَا شُوَاظٌۭ مِّن نَّارٍۢ وَنُحَاسٌۭ فَلَا تَنتَصِرَانِ
Anã sako wani harshe daga wata wutã a kanku, da narkakkiyar tagulla. To, bã zã ku nẽmi taimako ba?
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
فَإِذَا ٱنشَقَّتِ ٱلسَّمَآءُ فَكَانَتْ وَرْدَةًۭ كَٱلدِّهَانِ
Sa'an nan idan sama ta tsãge kuma ta zama jã kamar jar fãta.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
فَيَوْمَئِذٍۢ لَّا يُسْـَٔلُ عَن ذَنۢبِهِۦٓ إِنسٌۭ وَلَا جَآنٌّۭ
To, a ran nan bã zã a tambayi wani mutum laifinsa ba, kuma haka aljani.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
يُعْرَفُ ٱلْمُجْرِمُونَ بِسِيمَٰهُمْ فَيُؤْخَذُ بِٱلنَّوَٰصِى وَٱلْأَقْدَامِ
zã a iya sanin mãsu laifi da alãmarsu, sabõda haka sai a kãma kwarkaɗarsu da sãwãyensu.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
هَٰذِهِۦ جَهَنَّمُ ٱلَّتِى يُكَذِّبُ بِهَا ٱلْمُجْرِمُونَ
Wannan Jahannama ce wadda mãsu laifi ke ƙaryatãwa game da ita.
يَطُوفُونَ بَيْنَهَا وَبَيْنَ حَمِيمٍ ءَانٍۢ
Sunã kẽwaya a tsakaninta da ruwan ɗimi mai tsananin tafasa.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
وَلِمَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ جَنَّتَانِ
Kuma wanda ya ji tsõron tsayãwa a gaba ga Ubangijinsa yanã da Aljanna biyu.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
ذَوَاتَآ أَفْنَانٍۢ
Mãsu rassan itãce.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
فِيهِمَا عَيْنَانِ تَجْرِيَانِ
A cikinsu akwai marẽmari biyu sunã gudãna.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
فِيهِمَا مِن كُلِّ فَٰكِهَةٍۢ زَوْجَانِ
A cikinsu akwai nau'i biyu daga kõwane 'ya'yan itãcen marmari.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
مُتَّكِـِٔينَ عَلَىٰ فُرُشٍۭ بَطَآئِنُهَا مِنْ إِسْتَبْرَقٍۢ ۚ وَجَنَى ٱلْجَنَّتَيْنِ دَانٍۢ
Sunã gincire a kan waɗansu shimfiɗu cikinsu tufãfin alharĩni mai kauri ne kuma nũnannun 'yã'yan itãcen Aljannar biyu kusakusa suke.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
فِيهِنَّ قَٰصِرَٰتُ ٱلطَّرْفِ لَمْ يَطْمِثْهُنَّ إِنسٌۭ قَبْلَهُمْ وَلَا جَآنٌّۭ
A cikinsu akwai mãtã mãsu taƙaita ganinsu, wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗebe budurcinsu ba kuma haka wani aljani.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
كَأَنَّهُنَّ ٱلْيَاقُوتُ وَٱلْمَرْجَانُ
Kamar dai su yaƙũtu ne da murjãni.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
هَلْ جَزَآءُ ٱلْإِحْسَٰنِ إِلَّا ٱلْإِحْسَٰنُ
Shin, kyautatãwa nã da wani sakamako? (Ã'aha) fãce kyautatãwa.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
وَمِن دُونِهِمَا جَنَّتَانِ
Kuma baicinsu akwai waɗansu gidãjen Aljanna biyu.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
مُدْهَآمَّتَانِ
Mãsu duhun inuwa.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
فِيهِمَا عَيْنَانِ نَضَّاخَتَانِ
A cikinsu akwai marẽmari biyu masu kwarãrar ruwa.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
فِيهِمَا فَٰكِهَةٌۭ وَنَخْلٌۭ وَرُمَّانٌۭ
A cikinsu akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno darummãni.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
فِيهِنَّ خَيْرَٰتٌ حِسَانٌۭ
A cikinsu, akwai wasu mãtã mãsu kyaun hãlãye, mãsu kyaun halitta.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
حُورٌۭ مَّقْصُورَٰتٌۭ فِى ٱلْخِيَامِ
Mãsu farin idãnu da baƙinsu waɗanda aka tsare a cikin haimõmi.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
لَمْ يَطْمِثْهُنَّ إِنسٌۭ قَبْلَهُمْ وَلَا جَآنٌّۭ
Wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗẽbe budurcinsu ba, kuma haka wani aljani.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
مُتَّكِـِٔينَ عَلَىٰ رَفْرَفٍ خُضْرٍۢ وَعَبْقَرِىٍّ حِسَانٍۢ
Sunã gincire a kan wasu matãsai mãsu kõren launi da katĩfun Abkara kyãwãwa.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
تَبَٰرَكَ ٱسْمُ رَبِّكَ ذِى ٱلْجَلَٰلِ وَٱلْإِكْرَامِ
Sũnan Ubangjinka, Mai girman Jalãla da Karimci, ya tsarkaka.
Surah 56: Al-Waqia — الواقعة
إِذَا وَقَعَتِ ٱلْوَاقِعَةُ
Idan mai aukuwa ta auku.
لَيْسَ لِوَقْعَتِهَا كَاذِبَةٌ
Bãbu wani (rai) mai ƙaryatãwa ga aukuwarta.
خَافِضَةٌۭ رَّافِعَةٌ
(Ita) mai ƙasƙantãwa ce, mai ɗaukakãwa.
إِذَا رُجَّتِ ٱلْأَرْضُ رَجًّۭا
Idan aka girgiza ƙasã girgizwa.
وَبُسَّتِ ٱلْجِبَالُ بَسًّۭا
Kuma aka niƙe duwãtsu, niƙẽwa.
فَكَانَتْ هَبَآءًۭ مُّنۢبَثًّۭا
Sai suka kasance ƙũra da ake wãtsarwa.
وَكُنتُمْ أَزْوَٰجًۭا ثَلَٰثَةًۭ
Kuma kun kasance nau'i uku.
فَأَصْحَٰبُ ٱلْمَيْمَنَةِ مَآ أَصْحَٰبُ ٱلْمَيْمَنَةِ
Watau mazõwa dãma. Mẽne ne mazõwa dãma?
وَأَصْحَٰبُ ٱلْمَشْـَٔمَةِ مَآ أَصْحَٰبُ ٱلْمَشْـَٔمَةِ
Da mazõwa hagu. Mẽne ne mazõwa hagu?
وَٱلسَّٰبِقُونَ ٱلسَّٰبِقُونَ
Da waɗanda suka tsẽre. Sũ wɗanda suka tsẽren nan,
أُو۟لَٰٓئِكَ ٱلْمُقَرَّبُونَ
Waɗancan, sũ ne waɗanda aka kusantar.
فِى جَنَّٰتِ ٱلنَّعِيمِ
A ckin Aljannar ni'ima.
ثُلَّةٌۭ مِّنَ ٱلْأَوَّلِينَ
Jama'a ne daga mutãnen farko.
وَقَلِيلٌۭ مِّنَ ٱلْءَاخِرِينَ
Da kaɗan daga mutãnen ƙarshe.
عَلَىٰ سُرُرٍۢ مَّوْضُونَةٍۢ
(Sunã) a kan wasu gadãje sãƙaƙƙuu.
مُّتَّكِـِٔينَ عَلَيْهَا مُتَقَٰبِلِينَ
Sunã gincire a kansu, sunã mãsu kallon jũna.
يَطُوفُ عَلَيْهِمْ وِلْدَٰنٌۭ مُّخَلَّدُونَ
Wasu yara samãri na dindindin gẽwaya a kansu.
بِأَكْوَابٍۢ وَأَبَارِيقَ وَكَأْسٍۢ مِّن مَّعِينٍۢ
Da wasu kõfuna da shantula da hinjãlai daga (giya) mai ɓuɓɓuga.
لَّا يُصَدَّعُونَ عَنْهَا وَلَا يُنزِفُونَ
Bã a sanya musu cĩwon jirĩ sabõda ita, kuma bã su buguwa.
وَفَٰكِهَةٍۢ مِّمَّا يَتَخَيَّرُونَ
Da wasu 'ya'yan itãcen marmari daga irin waɗanda suke zãɓe.
وَلَحْمِ طَيْرٍۢ مِّمَّا يَشْتَهُونَ
Da nãman tsuntsãye daga wanda suke ganin sha'awa.
وَحُورٌ عِينٌۭ
Da wasu mãtã mãsu fararen idanu da girmansu.
كَأَمْثَٰلِ ٱللُّؤْلُؤِ ٱلْمَكْنُونِ
Kamar misãlan lu'ulu'u wanda aka ɓõye.
جَزَآءًۢ بِمَا كَانُوا۟ يَعْمَلُونَ
A kan sakamakon, dõmin abin da suka kasance sunã aikatãwa.
لَا يَسْمَعُونَ فِيهَا لَغْوًۭا وَلَا تَأْثِيمًا
Bã su jin wata yãsassar magana a cikinta, kuma bã su jin sun yi laifi.
إِلَّا قِيلًۭا سَلَٰمًۭا سَلَٰمًۭا
Sai dai wata magana (mai dãɗi): Salãmun, Salãmun.
وَأَصْحَٰبُ ٱلْيَمِينِ مَآ أَصْحَٰبُ ٱلْيَمِينِ
Da mazõwa dãma. Mẽne ne mazõwa dãma?
فِى سِدْرٍۢ مَّخْضُودٍۢ
(Sunã) a cikin itãcen magarya maras ƙaya.
وَطَلْحٍۢ مَّنضُودٍۢ
Da wata ayaba mai yawan 'ya'ya.
وَظِلٍّۢ مَّمْدُودٍۢ
Da wata inuwa mĩƙaƙƙiya.
وَمَآءٍۢ مَّسْكُوبٍۢ
Da wani ruwa mai gudãna.
وَفَٰكِهَةٍۢ كَثِيرَةٍۢ
Da wasu 'ya'yan itacen marmari mãsu yawa.
لَّا مَقْطُوعَةٍۢ وَلَا مَمْنُوعَةٍۢ
Bã su yankẽwa kuma bã a hana su.
وَفُرُشٍۢ مَّرْفُوعَةٍ
Da wasu shimfiɗu maɗaukaka.
إِنَّآ أَنشَأْنَٰهُنَّ إِنشَآءًۭ
Lalle Mũ, Mun ƙãga halittarsu ƙãgãwa.
فَجَعَلْنَٰهُنَّ أَبْكَارًا
Sa'an nan Muka sanya su budurwai.
عُرُبًا أَتْرَابًۭا
Mãsu son mazansu, a cikin tsãrã ɗaya.
لِّأَصْحَٰبِ ٱلْيَمِينِ
Ga mazõwa dãma.
ثُلَّةٌۭ مِّنَ ٱلْأَوَّلِينَ
Wata ƙungiya ce daga mutãnen farko.
وَثُلَّةٌۭ مِّنَ ٱلْءَاخِرِينَ
Da wata ƙungiya daga mutãnen ƙarshe.
وَأَصْحَٰبُ ٱلشِّمَالِ مَآ أَصْحَٰبُ ٱلشِّمَالِ
Mazõwa hagu, Mẽne ne mazõwa hagu?
فِى سَمُومٍۢ وَحَمِيمٍۢ
Sunã a cikin wata iskar zãfi da wani ruwan zãfi.
وَظِلٍّۢ مِّن يَحْمُومٍۢ
Da wata inuwa ta hayãƙi mai baƙi.
لَّا بَارِدٍۢ وَلَا كَرِيمٍ
Bã mai sanyi ba, kuma bã mai wata ni'ima ba.
إِنَّهُمْ كَانُوا۟ قَبْلَ ذَٰلِكَ مُتْرَفِينَ
Lalle sũ, sun kasance a gabãnin wannan waɗanda aka jiyar dãɗi.
وَكَانُوا۟ يُصِرُّونَ عَلَى ٱلْحِنثِ ٱلْعَظِيمِ
Kuma sun kasance sunã dõgẽwa a kan mummũnan zunubi mai girma.
وَكَانُوا۟ يَقُولُونَ أَئِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًۭا وَعِظَٰمًا أَءِنَّا لَمَبْعُوثُونَ
Kuma sun kasance sunã cẽwa: "Shin idan mun mutukuma muko kasance turɓãya da ƙasũsuwa shin lalle mũ waɗanda zã a kõma rãyarwa ne haƙĩƙatan?"
أَوَءَابَآؤُنَا ٱلْأَوَّلُونَ
"Shin, kuma da ubanninmu na farko?"
قُلْ إِنَّ ٱلْأَوَّلِينَ وَٱلْءَاخِرِينَ
Ka ce: "Lalle mutãnen farko da na ƙarshe."
لَمَجْمُوعُونَ إِلَىٰ مِيقَٰتِ يَوْمٍۢ مَّعْلُومٍۢ
"Tabbas, waɗanda ake tãrãwa ne a cikin wani yini sananne."
ثُمَّ إِنَّكُمْ أَيُّهَا ٱلضَّآلُّونَ ٱلْمُكَذِّبُونَ
"Sa'an nan lalle ku, ya kũ ɓatattu, mãsu ƙaryatãwa!"
لَءَاكِلُونَ مِن شَجَرٍۢ مِّن زَقُّومٍۢ
"Lalle mãsu cĩ ne daga wata itãciya ta zaƙƙum (ɗanyen wutã)."
فَمَالِـُٔونَ مِنْهَا ٱلْبُطُونَ
"Har za ku zama mãsu cika cikunna daga gare ta."
فَشَٰرِبُونَ عَلَيْهِ مِنَ ٱلْحَمِيمِ
"Sa'an nan kuma mãsu shã ne, a kan wannan abin cin, daga ruwan zãfi."
فَشَٰرِبُونَ شُرْبَ ٱلْهِيمِ
"Ku zama mãsu shã irin shan rãƙuma mãsu ƙishirwa."
هَٰذَا نُزُلُهُمْ يَوْمَ ٱلدِّينِ
Wannan ita ce liyãfarsu a rãnar sakamako.
نَحْنُ خَلَقْنَٰكُمْ فَلَوْلَا تُصَدِّقُونَ
Mũ ne Muka halitta ku, to, don me bã zã ku gaskata ba?
أَفَرَءَيْتُم مَّا تُمْنُونَ
Shin kuma kun ga abin da kuke fitarwa na maniyyi?
ءَأَنتُمْ تَخْلُقُونَهُۥٓ أَمْ نَحْنُ ٱلْخَٰلِقُونَ
Shin kũ ne kuke halitta shi, kõ kuwa mũ ne Mãsu halittãwa?
نَحْنُ قَدَّرْنَا بَيْنَكُمُ ٱلْمَوْتَ وَمَا نَحْنُ بِمَسْبُوقِينَ
Mũ ne Muka ƙaddara mutuwa a tsakãninku, kuma ba Mu zama Mãsu gajiyãwa ba,
عَلَىٰٓ أَن نُّبَدِّلَ أَمْثَٰلَكُمْ وَنُنشِئَكُمْ فِى مَا لَا تَعْلَمُونَ
A kan Mu musanya waɗansu (mutãne) kamarku, kuma Mu mayar da ku a cikin wata halitta da ba ku sani ba.
وَلَقَدْ عَلِمْتُمُ ٱلنَّشْأَةَ ٱلْأُولَىٰ فَلَوْلَا تَذَكَّرُونَ
Kuma lalle, ne haƙĩƙa, kun san halittar farko, to, don me ba zã ku yi tunãni ba?
أَفَرَءَيْتُم مَّا تَحْرُثُونَ
Shin, kuma kun ga abin da kũke nõmãwa?
ءَأَنتُمْ تَزْرَعُونَهُۥٓ أَمْ نَحْنُ ٱلزَّٰرِعُونَ
Shin, kũ ne ke tsirar da shi kõ kuwa Mũ ne Mãsu tsirarwa?
لَوْ نَشَآءُ لَجَعَلْنَٰهُ حُطَٰمًۭا فَظَلْتُمْ تَفَكَّهُونَ
Dã Munã so lalle, da Mun sanya shi bũsasshiyar ciyãwa, sai ku yini kunã mãmãkin bãƙin ciki.
إِنَّا لَمُغْرَمُونَ
(Kunã cẽwa) "Lalle haƙĩƙa an azã mana tãra!"
بَلْ نَحْنُ مَحْرُومُونَ
"Ã'a, mun dai zama waɗanda aka hanã wa!"
أَفَرَءَيْتُمُ ٱلْمَآءَ ٱلَّذِى تَشْرَبُونَ
Shin, kuma kun ga ruwa wannan da kuke sha?
ءَأَنتُمْ أَنزَلْتُمُوهُ مِنَ ٱلْمُزْنِ أَمْ نَحْنُ ٱلْمُنزِلُونَ
Shin, kũ ne kuke saukar da shi daga girgije, kõ kuwa Mũne Mãsu saukarwa?
لَوْ نَشَآءُ جَعَلْنَٰهُ أُجَاجًۭا فَلَوْلَا تَشْكُرُونَ
Dã Mun so, dã Mun mayar da shi ruwan zartsi. To don me bã ku gõdẽwa?
أَفَرَءَيْتُمُ ٱلنَّارَ ٱلَّتِى تُورُونَ
Shin, kuma kun ga wutã wannan da kuke ƙyastãwa?
ءَأَنتُمْ أَنشَأْتُمْ شَجَرَتَهَآ أَمْ نَحْنُ ٱلْمُنشِـُٔونَ
Shin, kũ ne kuke ƙagã halittar itãciyarta, kõ kuwa Mũ ne Mãsu ƙãgãwa?
نَحْنُ جَعَلْنَٰهَا تَذْكِرَةًۭ وَمَتَٰعًۭا لِّلْمُقْوِينَ
Mũ ne Muka sanya ta wata abar wa'azi da jin dãɗi ga matafiya a cikin jẽji.
فَسَبِّحْ بِٱسْمِ رَبِّكَ ٱلْعَظِيمِ
Sai ka tsarkake sũnan Ubangijinka Mai girma.
۞ فَلَآ أُقْسِمُ بِمَوَٰقِعِ ٱلنُّجُومِ
To, bã sai Na yi rantsuwa ba da lõkutan fãɗuwar taurãri.
وَإِنَّهُۥ لَقَسَمٌۭ لَّوْ تَعْلَمُونَ عَظِيمٌ
Kuma lalle ne' haƙĩƙa, rantsuwa ce mai girma, dã kun sani.
إِنَّهُۥ لَقُرْءَانٌۭ كَرِيمٌۭ
Lalle shi (wannan littãfi), haƙĩƙa, abin karantãwa ne mai daraja.
فِى كِتَٰبٍۢ مَّكْنُونٍۢ
A cikin wani littafi tsararre.
لَّا يَمَسُّهُۥٓ إِلَّا ٱلْمُطَهَّرُونَ
Bãbu mai shãfa shi fãce waɗanda aka tsarkake.
تَنزِيلٌۭ مِّن رَّبِّ ٱلْعَٰلَمِينَ
Wanda aka saukar ne daga Ubangijin halitta.
أَفَبِهَٰذَا ٱلْحَدِيثِ أَنتُم مُّدْهِنُونَ
Shin, to, wannan lãbãrin ne kuke mãsu wulãkantãwa?
وَتَجْعَلُونَ رِزْقَكُمْ أَنَّكُمْ تُكَذِّبُونَ
Kuma kunã sanya arzikinku (game da shi) lalle kũ, ku ƙaryata (shi)?
فَلَوْلَآ إِذَا بَلَغَتِ ٱلْحُلْقُومَ
To, don me idan rai ya kai ga maƙõshi? (Kusa da mutuwa).
وَأَنتُمْ حِينَئِذٍۢ تَنظُرُونَ
Alhãli kuwa kũ, a lõklcin nan, kunã kallo.
وَنَحْنُ أَقْرَبُ إِلَيْهِ مِنكُمْ وَلَٰكِن لَّا تُبْصِرُونَ
Kuma Mũ ne mafi kusanta gare shi daga gare ku, to, amma kũ bã ku gani.
فَلَوْلَآ إِن كُنتُمْ غَيْرَ مَدِينِينَ
To, don me in dai kun kasance bã waɗanda zã a yi wa sakamako ba?
تَرْجِعُونَهَآ إِن كُنتُمْ صَٰدِقِينَ
Ku mayar da shi (cikin jikinsa) har idan kun kasance mãsu gaskiya.
فَأَمَّآ إِن كَانَ مِنَ ٱلْمُقَرَّبِينَ
To, amma idan (mai mutuwar) ya kasance daga makusanta,
فَرَوْحٌۭ وَرَيْحَانٌۭ وَجَنَّتُ نَعِيمٍۢ
Sai hũtawa da kyakkyawan abinci da Aljannar ni'ima.
وَأَمَّآ إِن كَانَ مِنْ أَصْحَٰبِ ٱلْيَمِينِ
Kuma amma idan ya kasance daga mazõwa dãma,
فَسَلَٰمٌۭ لَّكَ مِنْ أَصْحَٰبِ ٱلْيَمِينِ
Sai (a ce masa) aminci ya tabbata a gare ka daga mazõwa dãma.
وَأَمَّآ إِن كَانَ مِنَ ٱلْمُكَذِّبِينَ ٱلضَّآلِّينَ
Kuma amma idan ya kasance daga mãsu ƙaryatãwar, ɓatattun,
فَنُزُلٌۭ مِّنْ حَمِيمٍۢ
Sai wata liyãfa ta ruwan zãfi.
وَتَصْلِيَةُ جَحِيمٍ
Da ƙõnuwa da Jahĩm,
إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ حَقُّ ٱلْيَقِينِ
Lalle wannan, haƙĩƙa, ita ce gaskiya ta yaƙĩni.
فَسَبِّحْ بِٱسْمِ رَبِّكَ ٱلْعَظِيمِ
Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangijinka, Mai karimci.
Surah 57: Al-Hadid — الحديد
سَبَّحَ لِلَّهِ مَا فِى ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ ۖ وَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلْحَكِيمُ
Abin da ke cikin sammai da ƙasa yã yi tasbĩhi ga Allah. Kuma Shĩ ne Mabuwãyi, Mai hikima.
لَهُۥ مُلْكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ ۖ يُحْىِۦ وَيُمِيتُ ۖ وَهُوَ عَلَىٰ كُلِّ شَىْءٍۢ قَدِيرٌ
Shĩ ne da mulkin sammai da ƙasa: Yanã rãyarwa kuma Yanã kashẽwa, kuma Shĩ Mai ikon yi ne a kan kõme.
هُوَ ٱلْأَوَّلُ وَٱلْءَاخِرُ وَٱلظَّٰهِرُ وَٱلْبَاطِنُ ۖ وَهُوَ بِكُلِّ شَىْءٍ عَلِيمٌ
Shĩ ne Na farko, Na ƙarshe, Bayyananne, Bõyayye, kuma Shĩ Masani ne ga dukkan kõme.
هُوَ ٱلَّذِى خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضَ فِى سِتَّةِ أَيَّامٍۢ ثُمَّ ٱسْتَوَىٰ عَلَى ٱلْعَرْشِ ۚ يَعْلَمُ مَا يَلِجُ فِى ٱلْأَرْضِ وَمَا يَخْرُجُ مِنْهَا وَمَا يَنزِلُ مِنَ ٱلسَّمَآءِ وَمَا يَعْرُجُ فِيهَا ۖ وَهُوَ مَعَكُمْ أَيْنَ مَا كُنتُمْ ۚ وَٱللَّهُ بِمَا تَعْمَلُونَ بَصِيرٌۭ
Shĩ ne wanda Ya halitta sammai da ƙasa a cikin wasu kwãnuka shida, sa'an nan Ya daidaitu a kan Al'arshi, Yanã sanin abin da ke shiga cikin ƙasa da abin da ke fita daga gare ta, da abin da ke sauka daga sama da abin da ke hawa cikinta, kuma Shĩ yanã tareda ku duk inda kuka kasance. Kuma Allah Mai gani ne ga abin da kuke aikatãwa.
لَّهُۥ مُلْكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ ۚ وَإِلَى ٱللَّهِ تُرْجَعُ ٱلْأُمُورُ
Shĩ ne da mulkin sammai da ƙasa, kuma zuwa gare Shĩ (Allah) kawai ake mayar da al'amura.
يُولِجُ ٱلَّيْلَ فِى ٱلنَّهَارِ وَيُولِجُ ٱلنَّهَارَ فِى ٱلَّيْلِ ۚ وَهُوَ عَلِيمٌۢ بِذَاتِ ٱلصُّدُورِ
Yanã shigar da dare a cikin yini, kuma Yanã shigar da yini a cikin dare, kuma Shi Masani ne ga abin da yake a cikin ƙirãza.
ءَامِنُوا۟ بِٱللَّهِ وَرَسُولِهِۦ وَأَنفِقُوا۟ مِمَّا جَعَلَكُم مُّسْتَخْلَفِينَ فِيهِ ۖ فَٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ مِنكُمْ وَأَنفَقُوا۟ لَهُمْ أَجْرٌۭ كَبِيرٌۭ
Ku yi ĩmãni da Allah da ManzonSa, kuma ku ciyar daga abin da Allah Ya wakilta ku a cikinsa (na dũkiya). To, waɗannan da suka yi ĩmãni daga cikinku, kuma suka ciyar, sunã da wani sakamako mai girma.
وَمَا لَكُمْ لَا تُؤْمِنُونَ بِٱللَّهِ ۙ وَٱلرَّسُولُ يَدْعُوكُمْ لِتُؤْمِنُوا۟ بِرَبِّكُمْ وَقَدْ أَخَذَ مِيثَٰقَكُمْ إِن كُنتُم مُّؤْمِنِينَ
kuma me ya same ku, bã zã ku yi ĩmãni ba da Allah, alhãli kuwa manzonSa na kiran ku dõmin ku yi ĩmãni da Ubangijinku, kuma lalle Allah Ya karɓi alkawarinku (cẽwa zã ku bauta Masa)? (Ku bauta Masa) idan kun kasance mãsu ĩmãni.
هُوَ ٱلَّذِى يُنَزِّلُ عَلَىٰ عَبْدِهِۦٓ ءَايَٰتٍۭ بَيِّنَٰتٍۢ لِّيُخْرِجَكُم مِّنَ ٱلظُّلُمَٰتِ إِلَى ٱلنُّورِ ۚ وَإِنَّ ٱللَّهَ بِكُمْ لَرَءُوفٌۭ رَّحِيمٌۭ
Shĩ ne wanda ke sassaukar da ãyõyi bayyanannu ga BãwanSa, dõmin Ya fitar da ku daga duffai zuwa ga haske, kuma lalle Allah haƙĩƙa Mai tausayi ne gare ku, Mai jin ƙai.
وَمَا لَكُمْ أَلَّا تُنفِقُوا۟ فِى سَبِيلِ ٱللَّهِ وَلِلَّهِ مِيرَٰثُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ ۚ لَا يَسْتَوِى مِنكُم مَّنْ أَنفَقَ مِن قَبْلِ ٱلْفَتْحِ وَقَٰتَلَ ۚ أُو۟لَٰٓئِكَ أَعْظَمُ دَرَجَةًۭ مِّنَ ٱلَّذِينَ أَنفَقُوا۟ مِنۢ بَعْدُ وَقَٰتَلُوا۟ ۚ وَكُلًّۭا وَعَدَ ٱللَّهُ ٱلْحُسْنَىٰ ۚ وَٱللَّهُ بِمَا تَعْمَلُونَ خَبِيرٌۭ
Kuma me ya sãme ku, bã zã ku ciyar ba dõmin ɗaukaka kalmar Allah, alhãli kuwa gãdon sammai da ƙasã na Allah ne? Wanda ya ciyar a gabãnin cin nasara, kuma ya yi yãƙi daga cikinku, bã ya zama daidai (da wanda bai yi haka ba). waɗancan ne mafĩfĩta girman daraja bisa ga waɗanda suka ciyar daga bãya kuma suka yi yãƙi. Kuma dukansu Allah Ya yi musu wa'adi da (sakamako) mai kyau, kuma Allah Masani ne ga abin da kuke aikatãwa.
مَّن ذَا ٱلَّذِى يُقْرِضُ ٱللَّهَ قَرْضًا حَسَنًۭا فَيُضَٰعِفَهُۥ لَهُۥ وَلَهُۥٓ أَجْرٌۭ كَرِيمٌۭ
Wãne ne wanda zai ranta wa Allah rance mai kyau dõmin Allah Ya ninka masa shi (a dũniya) kuma Yanã da wani sakamako na karimci (a Lãhira)?
يَوْمَ تَرَى ٱلْمُؤْمِنِينَ وَٱلْمُؤْمِنَٰتِ يَسْعَىٰ نُورُهُم بَيْنَ أَيْدِيهِمْ وَبِأَيْمَٰنِهِم بُشْرَىٰكُمُ ٱلْيَوْمَ جَنَّٰتٌۭ تَجْرِى مِن تَحْتِهَا ٱلْأَنْهَٰرُ خَٰلِدِينَ فِيهَا ۚ ذَٰلِكَ هُوَ ٱلْفَوْزُ ٱلْعَظِيمُ
Rãnar da zã ka ga mũminai maza da mũminai mãtã haskensu nã tafiya a gaba gare su, da kuma dãma gare su. (Anã ce musu) "Bushãrarku a yau, ita ce gidajen Aljanna." Ruwa na gudãna daga ƙarƙashinsu sunã mãsu dawwama a cikinsu. Wannan, shĩ ne babban rabo mai girma.
يَوْمَ يَقُولُ ٱلْمُنَٰفِقُونَ وَٱلْمُنَٰفِقَٰتُ لِلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ ٱنظُرُونَا نَقْتَبِسْ مِن نُّورِكُمْ قِيلَ ٱرْجِعُوا۟ وَرَآءَكُمْ فَٱلْتَمِسُوا۟ نُورًۭا فَضُرِبَ بَيْنَهُم بِسُورٍۢ لَّهُۥ بَابٌۢ بَاطِنُهُۥ فِيهِ ٱلرَّحْمَةُ وَظَٰهِرُهُۥ مِن قِبَلِهِ ٱلْعَذَابُ
Rãnar da munafikai maza da munãfikai mãtã ke cẽwa waɗanda suka yi ĩmãni: "Ku dũbẽ mu, mu yi makãmashi daga haskenku!" A ce (musu): "Ku kõma a bãyanku, dõmin ku nẽmo wani haske." Sai a danne a tsakãninsu da wani gãru yanã da wani ƙyaure, a cikinsa nan rahama take, kuma a bãyansa daga wajensa azaba take.
يُنَادُونَهُمْ أَلَمْ نَكُن مَّعَكُمْ ۖ قَالُوا۟ بَلَىٰ وَلَٰكِنَّكُمْ فَتَنتُمْ أَنفُسَكُمْ وَتَرَبَّصْتُمْ وَٱرْتَبْتُمْ وَغَرَّتْكُمُ ٱلْأَمَانِىُّ حَتَّىٰ جَآءَ أَمْرُ ٱللَّهِ وَغَرَّكُم بِٱللَّهِ ٱلْغَرُورُ
Sunã kiran su, "Ashe, bã tãre muke da ku ba?" Su ce: "Ĩ, amma kũ, kun fitini kanku, kuma kun yi jiran wata masĩfa, kuma kunyi shakka, kuma waɗansu gũrace-gũrace sun rũɗe ku, har umurnin Allah ya jẽ muku, kumamarũɗi ya rũɗe ku game da Allah."
فَٱلْيَوْمَ لَا يُؤْخَذُ مِنكُمْ فِدْيَةٌۭ وَلَا مِنَ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ ۚ مَأْوَىٰكُمُ ٱلنَّارُ ۖ هِىَ مَوْلَىٰكُمْ ۖ وَبِئْسَ ٱلْمَصِيرُ
"To, a yau bã zã a karɓi fansa daga gare ku ba. Kuma bã zã a karɓa daga waɗanda suka kãfirta ba. Makõmarku wutã ce, ita ce mai dacẽwa da ku, kuma makõmarku ɗin nan tã mũnana."
۞ أَلَمْ يَأْنِ لِلَّذِينَ ءَامَنُوٓا۟ أَن تَخْشَعَ قُلُوبُهُمْ لِذِكْرِ ٱللَّهِ وَمَا نَزَلَ مِنَ ٱلْحَقِّ وَلَا يَكُونُوا۟ كَٱلَّذِينَ أُوتُوا۟ ٱلْكِتَٰبَ مِن قَبْلُ فَطَالَ عَلَيْهِمُ ٱلْأَمَدُ فَقَسَتْ قُلُوبُهُمْ ۖ وَكَثِيرٌۭ مِّنْهُمْ فَٰسِقُونَ
Shin, lõkaci bai yi ba ga wa ɗanda suka yi ĩmãnĩ zukãtansu su yi tawãlu'i ga ambaton Allah da abin da ya sauka daga gaskiya? Kada su kasance kamar waɗanda aka bai wa littãfi a gabãnin haka, sai zãmani ya yi tsawo a kansu, sabõda haka zukãtansu suka ƙẽƙashe, kuma masu yawa daga cikinsu fãsiƙai ne.
ٱعْلَمُوٓا۟ أَنَّ ٱللَّهَ يُحْىِ ٱلْأَرْضَ بَعْدَ مَوْتِهَا ۚ قَدْ بَيَّنَّا لَكُمُ ٱلْءَايَٰتِ لَعَلَّكُمْ تَعْقِلُونَ
Ku sani cẽwa Allah Yanã rãyar da ƙasã a bãyan mutuwarta. Lalle Mun bayyanamuku ãyõyi da fatan zã ku yi hankali.
إِنَّ ٱلْمُصَّدِّقِينَ وَٱلْمُصَّدِّقَٰتِ وَأَقْرَضُوا۟ ٱللَّهَ قَرْضًا حَسَنًۭا يُضَٰعَفُ لَهُمْ وَلَهُمْ أَجْرٌۭ كَرِيمٌۭ
Lalle mãsu gaskatãwa maza da mãsu gaskatãwa mãtã, kuma suka ranta wa Allah rance mai kyau, anã riɓanya musu, kuma suna da wani sakamako na karimci.
وَٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ بِٱللَّهِ وَرُسُلِهِۦٓ أُو۟لَٰٓئِكَ هُمُ ٱلصِّدِّيقُونَ ۖ وَٱلشُّهَدَآءُ عِندَ رَبِّهِمْ لَهُمْ أَجْرُهُمْ وَنُورُهُمْ ۖ وَٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ وَكَذَّبُوا۟ بِـَٔايَٰتِنَآ أُو۟لَٰٓئِكَ أَصْحَٰبُ ٱلْجَحِيمِ
Kuma waɗanda suka yi ĩmãni da Allah da MazanninSa waɗannan sũ ne kamãlar gaskatãwa kuma su ne mãsu shahãda awurin Ubangjinsu. sunã da sakamakonsu da haskensu. waɗanda suka kafirta kuma suka ƙaryata game da ãyõyinMu, waɗannan su ne'yan Jahĩm.
ٱعْلَمُوٓا۟ أَنَّمَا ٱلْحَيَوٰةُ ٱلدُّنْيَا لَعِبٌۭ وَلَهْوٌۭ وَزِينَةٌۭ وَتَفَاخُرٌۢ بَيْنَكُمْ وَتَكَاثُرٌۭ فِى ٱلْأَمْوَٰلِ وَٱلْأَوْلَٰدِ ۖ كَمَثَلِ غَيْثٍ أَعْجَبَ ٱلْكُفَّارَ نَبَاتُهُۥ ثُمَّ يَهِيجُ فَتَرَىٰهُ مُصْفَرًّۭا ثُمَّ يَكُونُ حُطَٰمًۭا ۖ وَفِى ٱلْءَاخِرَةِ عَذَابٌۭ شَدِيدٌۭ وَمَغْفِرَةٌۭ مِّنَ ٱللَّهِ وَرِضْوَٰنٌۭ ۚ وَمَا ٱلْحَيَوٰةُ ٱلدُّنْيَآ إِلَّا مَتَٰعُ ٱلْغُرُورِ
Ku sani cẽwa rãyuwar dũniya wãsã ɗai ce da shagala da ƙawa da alafahri a tsakãninku da gãsar wadãta ta dũkiya da ɗiya, kamar misãlin shũka wadda yabanyarta ta bãyar da sha'awa ga manõma, sa'an nan ta ƙẽƙashe, har ka ganta tã zama rawaya sa'an nan ta kõma rauno. Kuma, alãmra akwai azãba mai tsanani da gãfara daga Allah da yarda. Kuma rãyuwar dũniya ba ta zama ba fãce ɗan jin dãɗin rũɗi kawai.
سَابِقُوٓا۟ إِلَىٰ مَغْفِرَةٍۢ مِّن رَّبِّكُمْ وَجَنَّةٍ عَرْضُهَا كَعَرْضِ ٱلسَّمَآءِ وَٱلْأَرْضِ أُعِدَّتْ لِلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ بِٱللَّهِ وَرُسُلِهِۦ ۚ ذَٰلِكَ فَضْلُ ٱللَّهِ يُؤْتِيهِ مَن يَشَآءُ ۚ وَٱللَّهُ ذُو ٱلْفَضْلِ ٱلْعَظِيمِ
Ku yi tsẽre zuwa ga (nẽman) gãfara daga Ubangjinku, da Aljanna fãɗinta kamar fãɗin samã da ƙasã ne, an yi tattalinta dõmin waɗanda suka yi ĩmãni da Allah da ManzanninSa. Wannan falalar Allah ce, Yanã bãyar da ita ga wanda Ya so. Kuma Allah Mai falala ne Mai girma.
مَآ أَصَابَ مِن مُّصِيبَةٍۢ فِى ٱلْأَرْضِ وَلَا فِىٓ أَنفُسِكُمْ إِلَّا فِى كِتَٰبٍۢ مِّن قَبْلِ أَن نَّبْرَأَهَآ ۚ إِنَّ ذَٰلِكَ عَلَى ٱللَّهِ يَسِيرٌۭ
Wata masifa bã zã ta auku ba a cikin ƙasã kõ a cikin rayukanku fãce tanã a cikin littãfi a gabãnin Mu halitta ta. Lalle wannan, ga Allah, mai sauƙi ne.
لِّكَيْلَا تَأْسَوْا۟ عَلَىٰ مَا فَاتَكُمْ وَلَا تَفْرَحُوا۟ بِمَآ ءَاتَىٰكُمْ ۗ وَٱللَّهُ لَا يُحِبُّ كُلَّ مُخْتَالٍۢ فَخُورٍ
Dõmin kada ku yi baƙin ciki a kan abin da ya kuɓuce muku, kuma kada ku yi mumar alfahari da abin da Ya bã ku. Kuma Allah bã Ya son dukkan mai tãƙama, mai alfahari.
ٱلَّذِينَ يَبْخَلُونَ وَيَأْمُرُونَ ٱلنَّاسَ بِٱلْبُخْلِ ۗ وَمَن يَتَوَلَّ فَإِنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلْغَنِىُّ ٱلْحَمِيدُ
Watau, waɗanda ke yin rõwa, kuma sunã umumin mutãne da yin rõwa. Kuma wanda ya jũya bãya, to, lalle Allah, Shĩ ne kaɗai Mawadãci, Gõdadde.
لَقَدْ أَرْسَلْنَا رُسُلَنَا بِٱلْبَيِّنَٰتِ وَأَنزَلْنَا مَعَهُمُ ٱلْكِتَٰبَ وَٱلْمِيزَانَ لِيَقُومَ ٱلنَّاسُ بِٱلْقِسْطِ ۖ وَأَنزَلْنَا ٱلْحَدِيدَ فِيهِ بَأْسٌۭ شَدِيدٌۭ وَمَنَٰفِعُ لِلنَّاسِ وَلِيَعْلَمَ ٱللَّهُ مَن يَنصُرُهُۥ وَرُسُلَهُۥ بِٱلْغَيْبِ ۚ إِنَّ ٱللَّهَ قَوِىٌّ عَزِيزٌۭ
Haƙĩƙa, lalle Mun aiko ManzanninMu da hujjõji bayyanannu, kuma Muka saukar da Littãfi da sikẽli tãre da su dõmin mutãne su tsayu da ãdalci, kuma Mun saukar da baƙin ƙarfe, a cikinsa akwai cutarwa mai tsanani da amfãni ga mutãne, kuma dõmin Allah Ya san mai taimakonSa da ManzanninSa a fake. Lalle ne Allah Mai ƙarfi ne, Mabuwãyi.
وَلَقَدْ أَرْسَلْنَا نُوحًۭا وَإِبْرَٰهِيمَ وَجَعَلْنَا فِى ذُرِّيَّتِهِمَا ٱلنُّبُوَّةَ وَٱلْكِتَٰبَ ۖ فَمِنْهُم مُّهْتَدٍۢ ۖ وَكَثِيرٌۭ مِّنْهُمْ فَٰسِقُونَ
Kuma haƙĩƙa, lalle, Mun aiki Nũhu da Ibrahĩm, kuma Muka sanya Annabci da Littĩfi a cikin zuriyarsu; daga cikinsu akwai mai nẽman shiryuwa, kuma mãsu yawa daga cikinsu fasiƙai ne.
ثُمَّ قَفَّيْنَا عَلَىٰٓ ءَاثَٰرِهِم بِرُسُلِنَا وَقَفَّيْنَا بِعِيسَى ٱبْنِ مَرْيَمَ وَءَاتَيْنَٰهُ ٱلْإِنجِيلَ وَجَعَلْنَا فِى قُلُوبِ ٱلَّذِينَ ٱتَّبَعُوهُ رَأْفَةًۭ وَرَحْمَةًۭ وَرَهْبَانِيَّةً ٱبْتَدَعُوهَا مَا كَتَبْنَٰهَا عَلَيْهِمْ إِلَّا ٱبْتِغَآءَ رِضْوَٰنِ ٱللَّهِ فَمَا رَعَوْهَا حَقَّ رِعَايَتِهَا ۖ فَـَٔاتَيْنَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ مِنْهُمْ أَجْرَهُمْ ۖ وَكَثِيرٌۭ مِّنْهُمْ فَٰسِقُونَ
Sa'an nan Muka biyar a bãyansu da ManzanninMu; kuma Muka biyar da ĩsã ɗan Maryama, kuma Muka ba shi Linjila kuma Muka sanya tausayi da rahama a cikin zukãtan waɗanda suka bĩ shi, da ruhbãnanci wanda suka ƙãga, shi, ba Mu rubũta shi ba a kansu, fãce dai (Mun rubũta musu nẽman yardar Allah, sa'an nan ba su tsare shi haƙƙin tsarẽwarsa ba, sabõda haka Muka bai wa waɗanda suka yi ĩmãni daga cikinsu sakamakonsu kuma mãsu yawa daga cikinsu fãsiƙai ne.
يَٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ ٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَءَامِنُوا۟ بِرَسُولِهِۦ يُؤْتِكُمْ كِفْلَيْنِ مِن رَّحْمَتِهِۦ وَيَجْعَل لَّكُمْ نُورًۭا تَمْشُونَ بِهِۦ وَيَغْفِرْ لَكُمْ ۚ وَٱللَّهُ غَفُورٌۭ رَّحِيمٌۭ
Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku bi Allah da taƙawa, ku yi ĩmãni da ManzonSa Ya bã ku rabo biyu daga rahamarSa, kuma Ya sanya muku wani haske wanda kuke yin tafiya da shi, kuma Ya gãfarta muku. Kuma Allah Mai gãfara ne, Mai rahama.
لِّئَلَّا يَعْلَمَ أَهْلُ ٱلْكِتَٰبِ أَلَّا يَقْدِرُونَ عَلَىٰ شَىْءٍۢ مِّن فَضْلِ ٱللَّهِ ۙ وَأَنَّ ٱلْفَضْلَ بِيَدِ ٱللَّهِ يُؤْتِيهِ مَن يَشَآءُ ۚ وَٱللَّهُ ذُو ٱلْفَضْلِ ٱلْعَظِيمِ
Dõmin kada mutãnen Littãfi su san cẽwa lalle bã su da ikon yi ga kõme na falalar Allah, kuma ita falalar ga hannun Allah kawai take, Yanã bãyar da ita ga wanda Ya so (wannan jãhilci yã hana su ĩmani). Kuma Al1ah Mai falala ne mai girma.