بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ
Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.
إِذَا جَآءَ نَصْرُ ٱللَّهِ وَٱلْفَتْحُ
Idan taimakon Allah ya zo da cin nasara.
وَرَأَيْتَ ٱلنَّاسَ يَدْخُلُونَ فِى دِينِ ٱللَّهِ أَفْوَاجًۭا
Kuma ka ga mutane suna shiga addinin Allah, ƙungiya-ƙungiya.
فَسَبِّحْ بِحَمْدِ رَبِّكَ وَٱسْتَغْفِرْهُ ۚ إِنَّهُۥ كَانَ تَوَّابًۢا
To, ka yi tasbihi game da gõde wa Ubangijinka, kuma ka nẽme Shi gafara, lalle Shi (Ubangijinka) Ya kasance Mai karɓar tũba ne.